Monday 25 February 2013

SHAYE SHAYEN MAGUNGUNA MASU FITAR DA MUTANE DA GA HAYACINSU

If there are images in this attachment, they will not be displayed.  Download the original attachment
 
A cikin shekarar da ya wuce ne yan uwa da abokan arziki suka yi dafifi zuwa garin Katsina auren Ali da Mabruka.Biki son kowa kin wanda ya rasa. Amarya da ango sun dace suna ta soyyayarsu irin ta kuruciya.Ba a shekara ba sai ga Mabruka ta dawo gida da kayanta karkaf da jiki duk raunuka.Binciken iyaye ya nuna cewa ango da amarya suna son junansu ama da yake suna zaune a gidan gado ne wasu kanen Ali su ka adabi gidan da sace sace da kuma shaye shaye.Ko takalmi Mabruka ta bari a waje ya tafi kenan gashi idan suka yi shaye shayen idanuwan su ba sa kallon kowa da gashi a ka har ya kai suka dake ta.Wannan labari  ya daga wa jamaa hankali ba dan komai ba sai dan kanen Ali’n nan duk mata ne kuma ba wace shekarunta ya wuce 24.Guda biyu yan makaranta ne daya kuma bazzawara.A kamaninsu da kyar a gane.Mahaifiyarsu ta yi iyaka kokarinta ta gane me ke sa su hauka wani lokaci wani lokaci kuma dacin rai ta kasa ganewa,bata ganin su da giya, kwayoyi ko taba.Anyi musu ruqiya dan Kore jinnu shiru.
Wannan matsala ya zama ruwan dare yanzu a al ummar mu.Bahaushe na cewa rashin sani shi ne cuta,abun da ba a gane shi ba ai ba ranar maganin shi.Ama a yanzu yawan aukuwar birkicewan jamaa ya sa an fara gane matsalolin.A da idan aka ga mutum na wasu halaye marasa kan gado sai a ce yana shan giya, wiwi ko hodar iblis;gaba gaba kwayoyi suka zo suka yi karfi irin su LSD,ecstasy,meth,mai reverse,duniya komai level da dai sauransu.
Yanzu babu alamari mai daga hankali Kaman cewa maganin da aka fi amfani da shi wurin fita daga hayaci da maye magani ne da ake samu a kusan kowane gida.magani ne da ko dan shekara goma ya shiga chemist za a bashi tunda magani ne da a da baya bukatar takardan likita.Nigeria kuma kasa ce da babu doka saboda haka mutum zai iya samun ko guda nawa ya ke so a kusan kowane lokaci. Masu shan wayannan magani ana kiransu yan parkalin,yan tutolin,yan benylin ,yan codeine ko kuma slow.
Mura dai ciwo ne da kusan kowa na yi a kalla sau hudu a shekara,saboda haka sayar da maganin mura dinnan ya zama dole .Matsalar shi ne yanda wasu suke bata shi mayar da shi abun sa maye. Yawancin maganin mura idan kuka duba za ku ga cewa suna maganin murar,tari,zazzabin murar ta hanyar sa mutum barci ko kuma ya rage wa mutum zafin nama. Jikin mutum sai ya dan yi sanyi wasu kuma su yi ta barci idan sun sha.
A cikin hirar da na yi da Mal Idris a Unguwar rimin Kaduna ya bayyana mana cewa yawancin masu shan maganin nan dan suyi barci ne ko su manta matsalolin rayuwa.wasu kuma ji suke idan sun sha tamkar basu da wata matsala.Wasu kuma idan suka sha maganin murar ya kashe musu jiki sai su hada da wasu kwayoyi kuma daban da ke sa su jin waras irin su a rungumi zaki.Refnol,exol,roche,bashi,tramol wayanda duk kayan sa maye ne yawancinsu magungunan asibiti ne ama idan aka sha su ba a dai dai ba akwai matsala.Mal Idris ya dade yana wa matasa fada akan illolin shan kwayoyi kuma ya kan binciki sababbin salo da suke fitowa da su kullum.
Ba matasa kade ke shan wayannan magungunan ba  dan su samu su yi slow dinnan a yanda suke fada.Masifa ce da ba babba ba yaro, ma mace ba namiji ba mai kudi ba talaka.
A cikin hirar da muka yi da wasu yan sanda WCPL Evelyn da abokin aikinta sun bayyana mana cewa a chemist ba a sayar da magungunan nan haka sidan ama ana sayar da su ta bayan fage.Na tambayesu irin magungunan da ake yayin sha a gari yanzu sun yi mana bayanin cewa akwai mogadon ,refnol,exol,kofsil.Na kara tambayar su yanda suke gane masu shaye shayen nan? Sun yi min bayani da cewa ya danganta,wasu idan sun har hada magungunan sai barci,wasu kuma su yi slow din, wasu kuma su kara karfi da kuzari wasu kuma idan hadin ya kwacibe har yi suke Kaman masu farfadiya.Idan su ka samu irin yan shaye shayen nan wasu ana kaisu police station idan kuma sun rika ana kai su har kotu.Idan kotu ta yanke hukunci kuma takan daure mutum tun balanta idan shaye shayen ya hadu da wani babban cin mutunci Kaman cin zarafin wani,sata,hatsari, ji ma wani rauni,zagi,fada,ko ta da husuma.
Matsalar nan ta shaye shayen maganin da ke iya sa maye ba a kasar hausa ta fara ba;masifa ce da akwai ta a kowace kasar duniya,tun balanta a inda ake da akida ta mutunci sai a fake da shan wayannan magunguna a maimakon giya da su cocaine da wiwi.Wayannan magunguna basu da wani wari ko alaman an sha su sai dai dabiar wanda ya sha idan ya chanza an ga ba yanda yake kullum ba ko kuma idan bai sha ba yayi ta kunci ko fada da mutane.
Menene sakamakon shaye shayen maganin asibiti ba da dalili ba ko kuma a kan wata manufa daban da samun warkewar ciwo?In ji Dr Ahmad Inuwa na Garko clinic Danladi Nasidi housing estate Kano ya ce, ‘’Hankali shi ne mutum .Idan mutum ba ya cikin hayacinsa ba abun da ba zai iya yi ba.A kiwon lafiya magungunan nan da aka mayar na maye ko zuga mutane suna da amfani sosai idan aka bi kaidar su; wasu na ciwon jiki ne wasu kuma maganin mura wasu na sa barci wasu kuma na hauka ne ma. Idan mutum yana amfani da su ba a bisa kaida ba sai ya zamanto jikin sa ya saba har ya zamanto kullum kwakwalwar sa na bukatar sai ya sha.Magungunan sun kasu kashi daban daban da akwai wayanda ake kira opiods irin su methadone ana amfani da su ne dan maganin zafin ciwo Kaman mumunar rauni ko bayan an yi wa mutum theatre.Idan aka zarce da sha ya wuce kaida sai ya zamanto wa mutum farilla ya sha kuma zai yi koma menene dan ya samu.Shan su dayawa kuma yana iya kawo yankewar num fashi ko kuma mutuwa farad daya.”Likita ya yi mana bayani.
“Depressants kuma irin su diazepam,lorazepam da dai sauransu ana bada su a asibiti ne domin kwantar wa mutum da hankali da samo mishi sauki idan yana fama da fargaba ko kasa barci.Idan ya zama jiki kuma sai mutum ya sha kullum ya na sa yawan barci,rashin kuzari rudewa ,tabin hankali .Hadarin neman a daina sha ba da zuwa asibiti ba idan ya zama jiki kuma shi ne zai iya kawo lahani saboda haka idan an ga ne dan kwaya irin wannan magungunar ya ke sha a kai shi asibiti dan likita ya kulla da yanda za a raba mai sha da wannan halin.”
Abu Sufyan tsohon dan kwaya ne mai kokarin ya daina saboda haka sai naga ya kamata muji daga bakin sa me ke sa su shan maganin asibiti ba da dalili ko izinin likita ba me suke ji idan su kayi shaye shayen? ya wahalar daina sha  da kuma farashin magungunan.
Ya bayyana mana cewa,“Yawancin mutane wani damuwa ko baccin rai ke sa su su fara shaye shaye ko son samun wani Karin karfin jiki ko karfin guiwa idan za su je wani wuri ko za su yi wani muhimmin abu ama daga baya sai ya zamanto wa mutum jiki kuma ko nawa ne zai sa kudi ya saya.Magungunan basu da tsada irin su lara,d5,diyaga,assage,fashion duk daga naira 10 ne zuwa naira 30.Masu tsada irin su babban tramol ne wanda ake sayar wa N200.magungunan mura kuma daga N150 ne ama original daga N500 su ke.Gaskiya daina sha na da wuya domin matsalolin rayuwa dayawa.kwayan diyaga guda daya da ake sayarwa N20 sai ya warware maka duk wani damuwa da kake ciki.”Abu Sufyan.
Samari,yan mata da matan aure sun fi zake wa a wurin shan maganin mura dan maye ,idan aka je wasu wuraren shakatawa wayanda yan mata da samari ke zagayawa a dare guda sai a samu kwalban magani 100 a lokaci guda.Budurwa daya ana iya samun kwalba 5 a jakanta.Wasu matan auren kuma haka su ma suke tara kwalaben magungunan nan su yi ta sha sun mayar da shi Kaman sobo.
Ina iyayen da ke ba yaransu kudi su je su sha shisha?to su ma su kula domin shisha grade B magunguna ake sawa aciki kar yaran ku su tashi daga grade A wanda kanshi suke zuka ko kuma su koma grade C wanda wiwi ake sawa a ciki.
Wasu na fakewa da cewa shan magani ba haramun bane tunda ba giya bane.wannan babban kuskure ne domin babbu addinin da zai yarda da mutum ya sa kansa a hali na maye ko bata rayuwarsa.Magani kyan sa mutum ya sha iyyaka kai’dan da masana su ka bada ba wai ka ji labarin wani kwaya na sa barci ka kama sha ba kulla ba.
Maganin wannan illa kuma na farko shi ne fadakarwa,idan jamaa duk aka farga za a iya sa ido domin samun maganin wanan musiba da buwayi al-umma.a rika kulawa da yara da irin mutanen da suke muammala da.Idan an ga chanjin yanayi ko da mutum ya karyata shan kwaya haka siddan a je asibiti a bincika.

Sanjay da bishiyar Goba


SANJAY DA BISHIYAN GOBA

Ma su kallon fim din india dai sun san mutan India da nuna soyayya,bajinta da kuma rashin yafiya idan aka yi musu laifi tun balanta idan laifin ya taba mutuncinsu.

A  shekarar da ta gabata ne kafofin yada labarai na India suka kawo labarin wani dan tahaliki mai suna Sanjay.

Sanjay dai   an bada labarin cewa shekarunsa 25 ne kuma dan kauyen Ramgaon,Vinasi ne ama yana aiki a babban birnin Mumbai.Ya yi aure da wata mai suna Tara kimanin shekara daya.A  ranar 9 ga watan Maris Sanjay ya dawo gida daga aiki kafin lokacin tashin sa yayi,sai ya tarar da matarsa a cikin halin da bai kamata ba da wani makwabcinsu anan cikin gidan Sanjay din.Rigima ya kaure har sai da aka koma kauye yin sharia.

Zuwa kauye sai ya zamanto bai kawo karshen rigimar ba domin ita Tara bata ba wa mijinta hakurin cin amanarsa da ta yi ba.Malam Sanjay da ya ga ta ki ba shi hakuri bayan yan uwansu sun shiga maganar domin warwareta ya sa Sanjay ya zuciya ya hau kan wata bishiyar goba da ke nan kusa da gidan iyayen sa.  

A cikin watan disamba na shekarar 2012 dai Sanjay watan sa tara  a kan wannan bishiyar domin Tara dai bata ba shi hakuri ba kuma ta hada kayanta ta koma birni wato Mumbai bata daka ta tashi ba.

Kanwar Sanjay mai suna Nisha ta tabbatar wa jaridar Asian Age na India da aukuwar wannan abu;ta kuma kara bayani cewa yayan nata a kan bishiyar yake yin komai, anan yake cin abinci, anan yake barci ,anan kuma yake yin bawali da bahaya.Da farkon zaman sa kan bishiyar ya’yan itacen kawai yake ci ama daga baya mahaifiyarsu na kai mishi abinci.

A nan abun tambaya shi ne;zuciyar me ya sa shi zaman kan bishiyar?Idan ta ba shi hakuri me zai kara mishi?

Tambaya na biyu kuma shi ne; yana yaji ne akan yana son matar tasa ta ba shi hakuri su koma zaman auren su haka?

Friday 18 January 2013

KISHI KUMALON MATA



                                          
Masu iya Magana suna fadin cewa duk macen da ba ta da kishi to bata cika mace ba ta rako mata duniya ne.Wai mata kadai ke da kishi?.Mene ne kishi kuma me nene mahimmancin sa a rayuwar dan adam.Kishi dai shi ne mutum ya ji rashin dadi da zaman wani ko samun sa ko zamantakewar sa ko ta hanyar soyaya,ko abun duniya ko ilimi ,ko kasuwa ko girma a wuri.Kishi kuma zai iya zama cewa mutum ya razana da shigar wani rayuwarsa ko rayuwar  wani ko wata da suke da kusanci ko kuma hanyar samu. Wata ya’ya ta tana cewa ko almajiran da suke layi karban sadaqa a kan titi ana samun kishi da hassada a tsakaninsu.Kishi ya dauko asali tun halartar dan adam, ba sabon abu bane ba kuma abu bane da za a ce yana da karshe ba sai dai a samu saukinsa da kuma halaya da ke zama daban  daban.
A kan kishi mutane dayawa sun halaka a duniya kuma dayawa za su halaka a lahira.Me nene halarcin kishi a addini?Halal ne ko haram,malamai sun yi bayani akan kishin da ya halarta shi ne kishi a wajen yawan ibada da kusanci da ubangiji.
A duk sanda mutum ya fita daga gida ya zaga unguwa,ko kuma ya saurari kafofin sadarwa idan yau ba ka ji ba, gobe ka ji wani mumunan aikin da kishi ya kawo.A ranar 6-9-12 labarun yahoo na yanar gizo ya kawo labarin wani dan wasan kwalon kafa a kasar ingila da ya kashe budurwarsa yar shekara goma sha biyar  domin kishi.A cikin watan da ya wuce ne na ga wata mata da budurwar mijinta ta bi ta har gida ta kama ta da kokawa, ta kwasa da gudu  budurwar ta hangi ruwan zafi ana dafawa a gefe ta dauka ta watsa a bayan matar nan,wa yanda suka san labarin sun tabbatar da cewa budurwar har a yau basu rabu da mutumin ba, mata ita ko jinya bai kare ba.
Maza na lahanta ko kashe abokan gaban su a wurin neman dukiya;a kasuwanci ,sarauta ,siyasa,aikin office ,soyayya da sauransu. Mata ma  na nasu kokarin a wurin kishi tun balanta a wurin soyyaya ko aure .Wata babbar mace da muka yi hira da ita a Abuja tayi mana tadin wata mata da budurwar mijinta ta biya yan fashi dasu tare matar a hanya su kashe ta domin mijin ya ki aurenta kuma a tunanin budurwar lefin matar ta gida ne.Maman Hauwa ta yi mana bayani cewa,”wata mata ce a nan garin Abuja mijin ta na da kudi da mulki sai ya zamanto cewa akwai budurwar da suka dade tare ama bai aure ta ba,da matan da budurwar duk sun yi iyaka kokarinsu a wajen malamai,bokaye,pastoci da dai sauran masu ba da taimako.Idan ita budurwar ta nemi samun kan mutumin sai matar ita ma ta zaga ta rusa.To a haka ne budurwar abun ya ishe ta ta ga gara ta aika ta lahira ta huta gabadaya.
A zahiri babu wanda zai so a ce wani ya fi shi a wani abu,ko kuma an fi son wani a kan sa,ko abun da mallakar ka kai kadai ne yau an wayi gari sai dai ku yi taraya da wani a kai.
Asalin wannan rubutu ya taso ne da na samu labarin kishiyar kanwata Allah ya yi mata rasuwa. Ita kanta kanwar nan tawa Binta na yi shekaru ban gan ta ba dan nisan garin da ta ke aure ama tare muka taso a ka yi mana aure.  San da ta aure  Isa  bai dade da fara aiki ba kuma ba shi da komai da sunan abun duniya,ba ta kaunarsa ko kadan ama ta bi umarnin iyaye ta aure shi kuma ta zauna.Isa ya taba aure har da da daya sai suka rabu da matarsa ,ganin ba zai zauna haka ba ya sa a nemo mishi wata ya aura.Aka hada shi da Binta suka yi aure.Abun da ya daure wa mutane kai shi ne,ita Binta tana da zafin kishi da gasa,ba ta son kowa ya fi ta da komai. Abun mamaki sai ya zamanto ita da kanta ta nemi matar mijin ta na da suke zumunci.Isa  ya nuna ba ya so ama bata daina ba har wata rana matar mijin ma ta zo gidanta suna hira Isa ya dawo gida kwatsam. Ita Binta ce ta boye matar nan ta shi a dakin ta a cikin wardrobe. Shekara da shekaru suka wuce Allah ya albarkaci zamansu da yaya  da rufin asiri.A wannan lokacin ne Isa ya kawo maganar yin aure.Abu na dangi ni da nake gefe labari na ji ama sai da na taya ta kishi tun balanta na ji an ce amarya ita                                                                                          za a kai abuja Binta ko an ajiye ta a gefe wai yaya sun yi mata yawa.yau sai aka wayi gari wai amaryar nan Allah ya dau kayan sa,Sai na ji kunya.Daukan dimin na mene ne,yau da Binta ce ta rasu ai  wannan baiwar Allah ita za ta rike mana yaya.Allah dai ya shirye mu ya ganar da mu.
Kowa ya san kishi ya san abun da yake iya jawo wa,abun da mutane dayawa ke   tambaya shi ne ta yaya za a rage kishi ko kuma a ci moriyar kishin nan? Ga mabiya addinin Islama da akwai adduoi da ake iya karantawa domin rage zafin kishi. Da akwai wasu hanyoyi da zamu iya amfani da su domin gane idan muna da kishi da ya wuce hankali da kuma yanda za mu rage zafin kishin. Ku biyo mu kashi na biyu na wannan rahoton wata mai zuwa domin karanta wayan nan hanyoyin.
Saadatu Hamma
 Kaduna
9-9-12