SANJAY
DA BISHIYAN GOBA
Ma su kallon
fim din india dai sun san mutan India da nuna soyayya,bajinta da kuma rashin
yafiya idan aka yi musu laifi tun balanta idan laifin ya taba mutuncinsu.
A shekarar da ta gabata ne kafofin yada labarai
na India suka kawo labarin wani dan tahaliki mai suna Sanjay.
Sanjay dai an bada
labarin cewa shekarunsa 25 ne kuma dan kauyen Ramgaon,Vinasi ne ama yana aiki a
babban birnin Mumbai.Ya yi aure da wata mai suna Tara kimanin shekara
daya.A ranar 9 ga watan Maris Sanjay ya dawo
gida daga aiki kafin lokacin tashin sa yayi,sai ya tarar da matarsa a cikin
halin da bai kamata ba da wani makwabcinsu anan cikin gidan Sanjay din.Rigima
ya kaure har sai da aka koma kauye yin sharia.
Zuwa kauye
sai ya zamanto bai kawo karshen rigimar ba domin ita Tara bata ba wa mijinta
hakurin cin amanarsa da ta yi ba.Malam Sanjay da ya ga ta ki ba shi hakuri
bayan yan uwansu sun shiga maganar domin warwareta ya sa Sanjay ya zuciya ya hau
kan wata bishiyar goba da ke nan kusa da gidan iyayen sa.
A cikin
watan disamba na shekarar 2012 dai Sanjay watan sa tara a kan wannan bishiyar domin Tara dai bata ba
shi hakuri ba kuma ta hada kayanta ta koma birni wato Mumbai bata daka ta tashi
ba.
Kanwar
Sanjay mai suna Nisha ta tabbatar wa jaridar Asian Age na India da aukuwar
wannan abu;ta kuma kara bayani cewa yayan nata a kan bishiyar yake yin komai,
anan yake cin abinci, anan yake barci ,anan kuma yake yin bawali da bahaya.Da
farkon zaman sa kan bishiyar ya’yan itacen kawai yake ci ama daga baya mahaifiyarsu
na kai mishi abinci.
A nan abun
tambaya shi ne;zuciyar me ya sa shi zaman kan bishiyar?Idan ta ba shi hakuri me
zai kara mishi?
Tambaya na
biyu kuma shi ne; yana yaji ne akan yana son matar tasa ta ba shi hakuri su
koma zaman auren su haka?
No comments:
Post a Comment